Tuesday, 6 November 2012

ILIMI SHINE GISHRIN RAYUWAR AL' UMMA


GABATARWA
Godiya ta tabbata ga Allah masanin abinda yake bayyane da kuma abinda yake boye, wanda ya fifita dan adam da Ilimi da aiki da ilimirisama da sukkan halitta.
Tsira da arpinci’ Allah sukara tabbata ga Shugaba Malaman duniya, da lahira Annabi Muhammad (SAW) da alayansa da sahabbansa da duk wanda ya bisu da gaskiya har izuwa rana al’kiyama.
Bayan haka, daga cikin irin falalar da Allah Tabaraka Wata’ala ya bawa ilimi yafi karfin kidayawa.
*                   Falalar ilimi wadda za’a iya hankalta a hankalce zakaga duk mutum in dai aka dangantashi da ilimi sakamakon wani abu da ya aikata sai yaji dadi kuma yayi farin ciki aransa, (ko da kuwa kungurmin jahili ne) saboda daraja da daukaka ta ilimi da Allah ya baiwa ilimi.
*                   Kuma yana daga cikin abinki da kyama irin na jahilci, duk mutum in dai aka dangantashi da jahilci sakamakon wani abu da ya aikata, sai yaji rashin jin dadi na karshe acikin ransa,(koda kuwa jahili ne).
*                   Dangane da falala da daukaka ta malamai akwai abubuwa guda (2) wadanda suka fi komai agurin ubangiji; Allah ya bayyana mana su acikin al’qur’ani, xayaacikin suratul Ali-imran :28, dayan acikin suratul Fadir: 18.

Arabic

Manzon Allah (S.A.W) yace “Ubangiji (S.W.T) zai tashi bayinsa ranar Al-kiyama, sannan kuma ya tashi malamai, sai yace “yaku taran malamai haqiqa ban sanya ilimi a garekuba sai domin sanina daku, kurna ban baku kyautar ilirni ba domin na azabtar daku, saboda haka ku tafi izuwa Al-jannah, haqiqa na gafarta muku”.
*       Kuma za muga irini ramukan da duhun jahilci yake tura jahilai.
Ina rokon ubangiji madaukakin sarki ya sanya wanna talifi ya zama mai amfani acikin rayuwarmu, mao kume amfanarwa ga al-umar muslim.
MENE NE MA’ANAR ILIMI?
Ilimi shine sanin wani abu wanda baka san shi ba.
MATSAYIN NEMAN ILIMI
Neman ilimi agurin dukkan musumi wajibine (dolene) saboda fadlin Manzon Allah(S.A.W)
Arabic

Fassara “Neman ilimi wajibine agurin dukkanin musulmi namiji da mace”
An farinlantawa musulmi neman ilimin abinda ke faruwa gareshi cikin halinsa (na rayuwa) a kowane hail yake, haqiqa babu makawa agareshi daga yin “SALLAH, AZUMI, ZAKKAH, HAJJ” yayin da ya wajaba akansa, hakanan hukuncin ciniki, idan shi dan kasuwane. To ya wajaba akansa ya nemi sani (ilimi) gwargwadon yadda zai bayar da wajibin. Malami suna cewa:

Arabic

“Duk abinda ya kasance wajibi baya cika sai tare dashi, to shima wannan abin ye zama wajibi”
Ubangiji Madaukakin Sarki ya fada acikin suratul Muhammada aya ta (19).
Arabic

Fassara “Kai sani ya (S.A. W) cewa haqiqa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah.....”
Imamush-shafl’i (R.A) sai yace “Sabida wajibcin ilimi sai Ubangiji ya fara da shi gabannin kalmar shahada.
Sannan kuma yazo acikin hadisil kudisi cewa Ubangiji mai girma da buwaya yace:
Arabic

“Kusanni kafin ku bauta mini yanzu idan baku sanniba; to yaya zaku iya bauta agareni?”
DARAJA DA FALALAR DA ALLAH YA BAWA ILIMI
Arabic

Ilimin mai ilimi da hankalin mai hankalin sunyi sabani wannan yana cewa “shi yafi don uwansa, wannan ma yana cewa shine yafi”


Arabic

Sai ilimi yace “kai hankali gayamin dani da kai wannene Ubangiji ya siffanta dashi yace yana dashi acikin al-qur’ani?
Arabic

Sai ta bayyana ga hankali, ya tabbata haqiqa ilimi shine shugabansa, saboda haka sai ya sunbaceshi yace shige gaba nabika, ya shugabana domin da ilimi Ubangiji ya siffantu.
1) Dangane da falalar ilimi da alherinsa da zamu fara lura da shi.
Allah madaukakin sarki da ya tashi halittar dan-adam, bai barshi haka sasakaiba sai dayayi shela, (akayi yekuwa) ya gayawa mala’iku kamar yadda yazo acikin al-qur’ani (acikin sural bakara) (Aya ta: 30-34).
Arabic

Ubangiji yayi wannan shela yace zai samar da halifa a doran kasa {wakili} wanda zai wakilci Allah (S.W.T) shi kuma wakili idan akace wanene, wakilin wane to duk kamar da zaka bawa wanda ya nadashi wakilcin to haka zaka bashi saboda komai zaiyi da duk abinda zai taflyar dashi, to da yawun wannan ya yakeyi.
To sai Allah yace “zai halicci wata halitta kuma zai bata wakilci”, wannan tasa mala’iku sukaji abinda nauyi, sukayi wani abu ‘bako’ sukaga cewar wannan makamin su yakamata ace su suke dashi. Amma ga Ubangiji (S.W.T) yace wata halitta zaiyi kuma ita zai bawa wannan makamin.
Saboda haka sai mala’iku suka nemi karin bayani suka ce:
Arabic

”Yanzu ya Ubangi (ka halicci wata halitta kabata wannan kima, ka ajiyeta ta zama wakiliyarka a duniya, Al-halin mugamu “Nusabbihu bi Hamdika wanukaddisu Lak” munayin tasbihi da godiya a gareka kuma muna tsarkakeka.
Sukuma wadancan da zaka basu wannan mukami fasadi zasuyi sudinga zubar da jini, to me Allah ya basu amsa.
Arabic

‘Ni nasan abinda baku saniba”
Saboda haka anan gurin Ubangiji Madaukakin Sarki da ilimi yayiwa mala’iku Tunkaho. Saboda haka wannan ya isa ace. ilimi yafi komai.
*       Sannan da Allah ya halicci Annabi Adamu (A.S) bai bashi karfin jiki wanda yafi nq mala’ikuba, baibashi karfi fiye da na mala’iku ba, baibashi sauri da hanzari flye dana mala’iku ba, da ya tashi sat yayi masa abu guda xaya(1) sai yace:
Arabic

“Na sanar da Adamu Sunayen Abubuwa dukkanninsu baki daya” wadanda ‘ya’yansa zasu yi amfani dashi. Wannan sunanta kwarya, wannan ludayi, wannan sunansa faifai, wannan ilimin sunansa Biology, Embiology, Geography. Duk wani ilimi da ake takama dashi a duniya a yau to sai da Allah ya sanar da Annabi Adamu shi, to da Ubangiji ya sanar dashi wannan ilimi, sai yace:
Arabic

“Sai Allah ya kawo abin akayi baje kolinsa aka bajewa mala’iku, Allah yace wa mala’iku ku gayamin sunan wadanan abubuwa inkun kasance ku masu gaskiyane, akan da’awarku to cewar ku kuka can-canta ku zama wakilaina a bayan kasa.” sai mala’iku sukace:
Arabic

“Tsarki ya tabbata gareka mu bamu da ilimi sai gwargwadon ilimin da kabamu kai ne Al-limu (Masani) kuma kai ne Al-Hakimu (Mai hikima) wanda kassan inda kake aje komainaka, domin da hikima kakeyi bada jahilciba, ba kuma da son zuciyaba.”
Saboda haka da mala’iku sukayi ikirari suka yadda da gajiyawarsu sai Allah yace:
Arabic

“Adamu gaya musu sunayen wadannan” ya dinga gaya musu, kazane wannan, wannan sunansa kaza, to bayan ya gama sanar dasu, sai Allah yace:
Arabic

“Allah yace bangaya mukuba nine nasan duk abinda yake boye acikin sama da kasa. To anan ma Allah da ilimi yayiwa mala’iku tunkaho” haqiqa kuma nine masani abinda kuke boyewa da abinda kuke fito dashi sarari. Saboda haka kuyi sujjada kugalda Annabi Adamu don kuwa shi malamunkune”

Arabic
“dukkannin mala’iku sukayi sujjada suka galda Annabi Adamu, sai dai shexan shine yaki yin sujjada yayi girman kai yace shi bazai gaida Adamu ba,” wannan kuma ta jawo masa bayan ya samu shekara 250,000, yana bin Allah,
Ubangiji ya la’anceshi ya koreshi daga cikin Al-jannah, wanda har abada bazai sake shigarta ba.
To wannan shi ya nuna mene falalar da ilimi, yake da ita domin dashi ne Ubangiji ya fifita Adamu (A.S) akan Mala’iku, ya kuma umarci mala’iku akan suyi sujjada sugaida Adamu (A.S).. A sanadin kin bi da rashin gaisheshi shexan yayi asarar kujerarsa, Ubangiji ya la’anceshi, kuma har abada bazai sami jin kaiba zai tabbata acikin ‘UMMUHU HAWIYA.’ Allah ka tsaremu ameen.
2) Kissar mutum da ya kashe mutum (100) sannan yayi nufin tuba tare da komawa ga Allah sai ya tambayi wani malami yadda zai tuba shi Allah zai karbi tubansa? Sai yabashi amsa da cewa Allah zai karbi tubansa, amma sai dai yayi hijira daga ganin xayake aciki ya koma izuwa wani garin daban. Saboda garin da yake ciki garin ashararan mutane ne, akan hanyarsa ta zuwa wancan garin da zai tuba sai mutuwa ta riskeshi a hanya saboda haka sai mala’ikun azaba suka zo zasu karbi ransa, sai kuma mala’ikun Rahama suma sukazo zasu karbi ransa, sai suka fara hujjataiya, mala’ikun Rahma suna cewa zuciyarsa ta karaya ya dawo zuwa ga Allah
Mala’ikun azaba suna cewa ”tunda yake baitaba aikin Alheri ba”, to sai Ubangiji ya aiko da Al-kalin mala’ika, akayi masa surar dan Adam, “domin mala’ika a surarsa ta mala’ika baya hukunci saboda shi ba wakilin Allah bane, dan Adam dai shine wakilin Allah, ko mala’ikane zai yi wani hukunci sai anmaida halittarsa irinta dan adam saboda girman da Allah yabawa dan adam shi kuma dan adam wannan ilimi da Allah ya bashi shine sirrin girman nasa.”
To sai mala’ikan yace a auna, idan yafi kusa da garin da ya baro na mutanen banza to mala’ikun azaba sai su dauki ransa idan kuma yafi kusa da garin da yayi nufin komawa saboda tuba to sai mala’ikun rahma su dau ransa, da akazo aunawa, sai Allah yayi wahayi cewar kasar da ya baro ta karanisa, wacce yayi nufin ta matso kusa, shikenan sai mala’ikun rahma akace su dau ransa, mutum (100) kashe dindi amma sai Allah yayi masa gafara dagy karaya.
Amma da ubangiji ya tashi sai yace:
Arabic

”Allah baya rahama baya jinkan ga wanda ya hada bautarsa da wani abu, ya mutum, da haka, wannan har abada Allah ba zaiji kansaba, yana gafara ga wasu laifukan wadanda bashirka ba.
Saboda haka zamuga babu abinda Allah yaki jini kuma ya tsana, irin shirka TAUHIDINNAN, (kadai tashi) dama kuma shi kadal ne, shi kadai ya fiso don haka da Allah ya tashi bayanin wannan abinda yafi muhimmanci agurinsa kuma yafi komai amfani agurin bayinsa sai yace: (acikin suratul Ali-imran: aya ta; 18).
Arabic
Allah ya shaida da kansa cewa babu abin bautawa da gaskiya saishi, shi kadaine, “WAHADAHULASHAPJKA LAHU.”
To da Allah ya kafa shaida akan abinda yafi komai kima da kansa, kuma sai ya nemi wasu shedun ya sake kafawa, kuma duk abinda yake da muhimmanci ana neman shaida akafa, sannan kuma awajan kafa sheda ana neman wanda shedarsa zata iya tsayawa, amma idan aka sami wanda shedarsa bazata iya tsayawa, ba ana zuwa za'a koreshi saboda rashin siffantuwa da sharadan karbar shaida, to saboda haka da Ubangiji ya tsashi kafa shaidu akan TAUHIDI, sai ya zabi siffar halitta guda biyu (2) ta farko sai yace: -
Arabic

“Mala’iku sun shaida haqiqa Allah shi kadai ne, ‘WAHADAHU LASHARIKA LAHU’ Saboda shedun Allah ne.”
To xayatashi kuma sai yace:
Arabic

“Haka masu ilimi suna shedun sane, ya sanyasu su zama shedunsa, akan cewa shi kadaine, “WAHADAHU LASHARIKA LAHU”
Saboda haka abinda yafi komai muhimmanci, sai aka nemo wadanda sukafi kowa aka sanyasu sheda saboda shaidar ta tsaya. (Idan shaida bata tsaya b, saboda haka abinda ake shaida akansa bazai tsaya ba).
To wannan shine Ubangiji madaukakin sarki ya nuna mana irin matsayinda ilimi yake dashi don haka Allah ya bawa masu wannan matsayi, matsayin su zama sune shedunsa a cikin halittarsa taba gaba daya.
3) Allah Madaukakin Sarki ya horewa Annabi Yusif (A.S) kyawu, irin na kakarsa Saratu, wannan kyawu na Annabi Yusif sai ya hadu da abubuwa guda biyu;
Tarbiya ta ruhi (wato imani cikikke).
Cikakken hankali da zurfin hankali, Annabi Yusif da wadannan abubuwa suka hadu agareshi, shi yasa matar da aka kaishi gurinta (wato uwar gijiyarsa) tunda ta ganshi saita fitunantu dashi, karshe ta dinga kewayawa ta dinga kewayan harta shirya abinda take bukata zai tabbata, da ranar tabbatar tazo shi kuma yaki, akarshe abubuwa suka bayyana, matan gari sukaji suka dinga yi mata habaici, ana sukanta, ana cewa: (acikin suratul yusif – ayata: 30).
Arabic
“Haqiqa matar sarki, taso yaron dakinta soyayya tariga ta kama zuciyarta, muna ganinta, acikin soyayya mabayyaniya.”
Shikenan da jin wannan, sai tace ni akewa wannan, to ban na shirya makirci, saboda haka sai ta shirya taron matan manyan mutane, ta zaunar dasu aka kawo tebura da komai, da abin yankawa, da wukake tace acigaba da yankamin zamuyi taro, data tabbatar tarko ya kamasu, duk sun shagala cikin aiki, sai tace da Annabi Yusif gashi na tara jama’a anata harkokin gida, gashi kai kuma kana gun xayazo kawuce mana kayi musu sannu. Sai yace to yana zuwa yawuce yace ”sannunku da aiki”, kowacce ta daga kai Allah yace: 
Arabic
Suna daga kai suka ganshi, sai suka girmamashi sukace tsarki ya tabbata ga Allah, wannan abu xayane kawai baza muce masaba, (shiba Allah bane) amma mala’ika ne, ba kuma na baya-baya ba ma cikin mala’iku yana cikin manya-manyansu.
Saboda haka Nana Zulaihat ta shigo sai tace:
Arabic

“Sai tace dasu jarabbabbun kawai, wannan saurayin shekara nawa yayi agurina banyi komai dashiba sai sau xaya amma gashi ku gani xayakawai gashi duk kun yanke hannunwanku, kutashi kubawa mutane guri.”
Sai sukace Yusifu sai ka amsawa uwar dakin taka ai tana da gaskiya. To da Annabi Yusif yaga abin ya rikice sai yace:
Arabic

“Ya Ubangi nafiso kakaini kurkuku domin na kubuta daga kaidin wadannan.”
To anan kaga kyan jiki, da kyan kira su suka kai Annabi Yusif (AS) kurkuku. Xayakaishi kurkuku, to me ya fito dashi? Shine ilimi.
Xayashiga kurkuku yana ta harkokinsa acikinta, sai wasu daga cikin mutanan fada laifi ya kawosu, su kaga anata girmamashi, sai sukace ya za’a yi haka mune kusa da sarki ba’a girmamamu sai wani wa-gairahum kawai, saboda haka ban muyi maganinsa, suna zuwa sai sukace sunyi mafarki xayayace yayi mafarki anyi masa wanka an mai dashi aiki, dayan yace “shi kuma yayi mafarkin towa akansa tsuntsaye suna tsattsaga, da suka gaya masa sai suka ce sunason ya fassara musu, to da ya tashi sai yace dasu. (ayata : 37)
Arabic
“Babu wani abinci da yake zuwa sai na fara gaya muku yadda za’ayi abincin, idan da daddare ne sai yace “gobe da safe abinci iri kaza za’ayi na karin kumallo, in anci abincin safe sai yace darana abunci iri kaza za’ayi, kuma sai suga irinsa akayi sai yace da daddare irin kaza za‘ayi, sai yace wannan labari da nake baku na abinci yana daga cikin ilimin da Ubangiji limitar dani.”
Saboda haka sai ya fara tsaramusu yayi ta kokarin ya jawosu kan tauhidi ya nuna musu shi ko dan gidan suwanene xayagama, sai yace to ga fassarar mafarkinku, kai za’ayi maka wanka ka koma kan aikinka, kai kuma za’a tsireka tsuntsaye sudinga cin namanka.
Sai suka ce ai karya muke ba mafarki mukayiba, sai yace:
Arabic

“Sai yace ai anriga angama tunda kuka tsokano, kuka roka, kukace a fassara muku to anriga angama baza ayanka ta tashiba.”
To shikenan kuwa abin ya tabbata. To dayan da zai futa sai yace dashi “UZUKURNI INDA RABRIK” in kaje ka gayawa sarki ubangidnka kace akwai wani bawan Allah acikin kurkuku da aka kamashi.
Annabi Yusif shikuma a matsayinsa na Annabi babba mai daraja, yayi abinda ake kiransa.
Arabic

Saboda haka sai Allah yabarshi ya mantar da wancan ya samu shekaru daga uku zuwa tara ya kara acikin kurkukun. Da Allah yayi nufin fitar dashi sai sarki yayi mafarki mai bantsoro aka rasa yadda za a fassara wannan mafarki to sai a lokacine wannan mutumin ya tuna da Annabi Yusif saiyace “ai kuwa akwai wani bawan Allah malamin gaske a kurkuku, a turani gurinsa zai iya fassara wannan mafarki, sai sukace jeka. Yana zuwa sai yace:
Arabic

“Ya kai Yusufu mai yawan gaskiya bamu labarin shanu guda bakwai kiba-kiba da kuma wasu bakwan ramammu, amma rammamun suka cinye masu kibar, akwai kuma zangarniyoyi guda bakwai wadanda suke koraye musa kyan gani, da kuma wasu bakwan busassu, sai masu bushewar suka darsu wadancan duka sumasuka kone. Aka gaya masa sai yace: “zakuyi shuka shekara bakwai abinci ya samu ya wadatu, daga nan kuma sai yunwa da fari su fadawa garin tsawon shekara bakwai.“
Da yaje yagayawa sarki kaji-kaji ya fassara mafarkin, sarki yace aje a gayamasa ya fito, da aka gaya masa ya fito sai yace ba zai fito ba, gashi dacan yace atunawa sarki, amma da akace ya fito sai yace bazai fitoba, saboda me? Saboda yana da ilimi, sai yace “a koma a tambayi matar nan da wadanda suka yayyanke hannu asanadin yace aje a tambayesu, to da aka koma aka tambayi mata, ita wannan imra’atil Azizi sai tace:
Arabic
“Yanzu gaskiya ta bayyana hakiqa nice na nemeshi shi kuma yaqi, haqika shi mai garkiya ne”
To anan annabi Yusif ya fito daga kurkuku afuwa akayi masa ko kuma me? Ba a yi masa afuwaba, to da ba ilimi sai ya fito, sai ace al-tafuwal malakine ya sameshi, (Sarki ne yayi masa afuwa amma wannan tuhuma tananan akansa). ”Kurkuku dai kyaleshi akayi.” To sai da ya nuna a iliminsa cewa inda akasan zaman takewa da ilimin siyasa to mutum bazai yadda da wannan ba, sai da aka tabbatar bada laifi ya shiga kurkuku, bisa kuskure ya shiga, wannan tuhumar babu ita akansa wankakkene, zaman da yayi a kurkuku, zamane na wani dalili amma ba laifin da ake tuntubarsa akansa ba, to sannan ya fito.
Yana fitowa yazo ya sami sarki malaman tarihi sukace da yazo fada sarki sai ya ganshi da karancin shekaru, sai yace “to bari in bige wannan yaron, sarki sai yayi masa wani yaren dama suna cikin sarakunan BUKUSUS. Da yazo yayi masa yare sai ya amsa da ya sake yi masa wani yaren sai ya sake amsawa ance sai da yayi masa yare daban-daban kala (70) duk Annabi Yusif yana amsasu, to saiAnnabi Yusif yayi wa sarki yare kala xayasarki sai ya kasa amsawa to shikenan sai sarki yace: (aya mta: 54).
Arabic

“Yau agurinmu kana da matsayi kana da mukami kuma yau kai amintaccen mune.”
Saboda haka sai yace:
Arabic

“Kadauki Treasurer na kasar gaba xayaka dan kata a hannuna domin ma da amana kuma inada tattalin arzikin da zan iya tafiyar da wannan al-amari ba tare da na sami karyewa ba,” saboda da wahalar da zakuzo ku shiga nan gaba idan ba mai Ilimi mai amana to ba wanda zai iya fitar daku, saboda haka sarki ya naxashi a matsayin babban ma’aji, to wannan shin yana nuna mana irin falalar da ilimi da masu ilimi suke dashi.
Annabi Yusif (A.S) kyan kirar jiki ta kaishi kurkuku, sannan kuma ilimi ya fito dashi, daga cikin kurkuku, sannan kuma ya xaurashi akan kujerar mulki wacce Allah yake cewa:
Arabic

“Allah ya xaura shi akan karagar mulki” ya samu mulki saboda haka da ilimi ya sami wannan”
4) Sannan wani abin da ilimi yake dashi shine: Ubangiji Maxaukakin Sarki ya tsara cewar duk wani abu da mutum yake dashi na duniya, idan ya dauka ya bayar to wannan abin ya ragu, amma banda ilimi, in dukkan mutanen duniya zasu taru kabasu ilimi to babu wani abu da zai ragu daga cikin ilimin ka sai daima ya karu.
5) Yana daga cikin abinda Allah ya bawa ilimi na baiwa da fifiqam (ba’a iya kwaceshi) misali duk abinda xan adam yake dashi ana iya kwace shi arabashi dashi amma banda ilimi, ko gwamnati ta kwaceshi tace ya zama nata, ko kuma wani ya kwaceshi da karfin tuwo, ya mirxe ka ya kwace abin da mutum yake dashi to shi ilimi ba’a yi masa haka.
6) Sannan kuma yana daga cikin fifiko na ilimi duk abinda Allah ya bawa wani nadaga baiwaAllah idan yaso baya shayi baya tsoro sai ya kwaceshi, amma Ubangiji ba yaiwa ilimi haka.
Misali idan Allah ya bawa mutum dukiya yana iya kwaceta, ya mai dashi talaka, sa dai adinga bada labari, ana cewa kaga da wanefa mai kuxine, amma yanzu ya zama bashida komai ya zama shawuya; Allah yana bawa mutum mulki ya qwace sai dai kaji ancewa wane “murabus” da mai mulkine amma yanzu sai dai na gidansa, Allah yana bawa mutum xa, ko ‘ya’ya, idan ya so sai ya karve su, saidai kaji ana cewa wane ya haifi ‘ya’ya kaza, amma yanzu bashi da ko da xayasun mutu, yana ba mutum mace ya aura ya karbe, yana ba mutum imani ya karbe, yana ba mutum iafiya ya karbe, amma in ya bashi abu xayatak baya karbewa wannan shine ilimi. Duk wanda Allah ya bawa ilimi ya bashi kenan bazai karbeba har ya mutu da kayansa, shiya sa Shugaba (S.A.W) yake cewa acikin wani hadisi ingantacce:
Arabic

“Allah baya kwace ilimi daga cikin zuciyar masu shi (ya kwaceshi, ya ciresshi ya barsu fanko), Allah baya haka, sai dai in yanason karbar ilimi sai ya karbi ran malami kawai.”
Arabic

“Idan Allah ya karbe ran masu ilimi, sai masu lilmi suka qare, kuma rayuwar duniya tana cike da mishkila, da bukatu iri daban-daban, da matsalaloli, da harkoki, su kuma suna da bukatar illmi” sai abar mutane cikin fagamniya idan sukazo sukayi fatawa ga jahilai sai a shir masu wanigurin (sai su amsa ba dai-dai ba) sai su bata su kuma batar saboda haka daganan bala’i ya abku.”
Wanda Imamu Ahmad bn Hambali (R.A) yake cewa xan adam yana da bukatar yaci abinci akalla sau xayaako wacce rana domin ya rayu batare da matsalaba, (ya Abukutada rayuwarsa daga halaka amma ilimi a yana bukatarsa a kowane fitar numfashi guda xaya domin za’aiya hisabi akan fitar wannan numfashi.
To anan Annabi (S.A.W) ya nusar damu abubuwa guda biyu (2)
i) Ya nuna mana ilimi Allah yana ladafawa masu shi yana tausasa musu yana tsarairayarsu, yana girmamasu baya yi musu abinda ya kewa kowa. Sannan kuma ya kare su daga baiwar da yayi musu baya kwaceta.
a) Shine Ibn Nasir yake cewa:
Yanzu irin duk gogewar da tafi tare kenan.
b) Idan masu dukiya sun gadarwa ‘ya’yansu dukiya da alfarma, ina mamakin tsyiyacewar ‘ya’yan malamai, idan basuyi karatuba sai dai adinga cewa dan malam ka qi halin malam.
ii) Sannan a wannan hadisi Shugaba (S.A.W) yana nuna cewa, rasa masu ilimi shine babban bala’i a duniya domin yana nuna alamar rugujewar duniya gabaki xayatazo, xan adam zai shiga cikin bala’i, domin duk abinda karasashi a duniya akan iya zama lafiya amma banda malami,duk randa aka rasa malamai to an shiga bala’i, duk sanka akan kabi Allah da irin qoqarinka akan bin Allah, duk irin fatawarka akan bin Allah, indai ba masu ilimi ne su kaje suka baka kaje kabi, to da qa’idarsu, gabaki xaya acikin bala’i zaku qare gobe alkiyama kuma ku tafi wuta, Allah ka kiya shemu ameen.
          Saboda haka Annabi (S.A.W) yana nuna mana falalar ilimi da masushi da kuma yadda ya kamata al’umma, su dinga kaffa-kaffa da masu ilimi idan suka kauce ayi qoqarin aga cewar wani ya komo gurin duk dadai cewar duk mai ilimin da ya kauce ba’a mai da gurbunsa, sai dai amai da qasa dashi, domin magaji, to wannan shine ya nuna mana irin falalar da ilimi yake dashi da kuma rayuwarsa shine alamar tashin duniya. Sannan har ila yau imamu Bukhari ya rawaito hadisi ta kan Anas bn Maliki cewa:
Arabic
“Yana daga cikin alamar tashin alkiyama da rugujewar duniya, shine a xauke ilimi ya zama masu xauke dashi sunyi qaranci, kuma jahilci ya maye ko’ina, kai harma a dinga tinka xashi.”
To wannan yana nuna mana duniya tazo karshe kuma komai zai ruguje ya lalace. Allah ya kiyayemu ameen.
7) Sannan shi ilimi yana daga cikin abinda Shugaba (SAW) yake cewa, Ubangiji Madaukakin Sarki shi yake zavar masu shi acikin hadin da yake cewa:
Arabic

“wanda duk Allah ya nufeshi da alheri to zai fahintar dashi addini”
Sai ya ce:
“Annabi (S.A.W) yace “Nine kasimu (mairabawa) Ubangi Allah koma shine mai bayarwa.”
To acikin wannan hadisin kuma akarshe Annabi yake cewa “duk juyin da za’a yi al’umar nan bazata zama cikin vataba, har qiyama tazo, ko kuma al’amarin Allah yazo”.
A wannan hadisin Shugaba (SAW) yana nuna mana “ALKHAIRUL MARBUBUN FIHI” al’heri da ake kwaxayi a sarnu shine ilimi, shi kuma baiwace wacce Allah yake zavar wanda yakeso ya bawa, sai ya bashi, shi Annabi (S.A.W) aikinsa shine ilimantarwa.
To kuma in anbida ilimi ba kuma kowanne yake da shiba, domin

Arabin
Dayawa akwai wanda yake iya haddace littafan fikihu, amma ba fakihi bane,
Arabin

Dayawa aikaga mutum yana tinqaho da ilimi sai ya xauki ilimi, ya kaishi gurin wanda ya yafishi fahimta.
Ita fahinta ba shaida bace ta satifiket, ta wata jami’a, ka sani shedar digiri, ko mastas, ko ka sani PHD, da sauransu, to duk wannan baya nuna cewar kasamu fikihu fiddin. Fikihu fiddini baiwace wacce Allah yake bayar da ita ga wanda yaso kawai, kuma yadda yaso haka yake bayar da ita.
To ita wanna baiwa ta “FIKIHU FIDDINI” Hujjatul Islam Imamu Gazzali ya fassarata da cewa “shine duk mai ilimin da ya yarda cewa lahira tafi duniya” to shine fikihu fiddin. Saboda haka zaka sameshi da aiki na gari, duniya bata dameshiba bata xaxashi da kasaba saboda yasan wal-qiyace kawai, da ta wuce shi kenan.
*       To shi wanda Allah ya bashi fikihu fiddin, a sanar dashi tafarkin aljannah dodar, ko sharafa yake, in zaka tambayeshi, da mai sharafa yana iya bayani, to zai maka bayanin yadda zaka shiga aljannah, saboda Allah yayi masa baiwa ta fahintar addini. Allah kayi mana wannan baiwar ameen.
*       Sannan yasan yadda zai tsira ya kuma san yadda zai tserar da waxansu.
*       Maganarsa zama take maganin tsatsar zukata, wanda suke fitar mugunya, yanzu da ya faxi magana sai yazama maganin wannan cutar.
*       Maganarsa zama take maganin talaucin zuciya, xayafaxi magana sai zuciya ta wadata ta zama wani abu a gurin Allah.
*       Sannan kuma yasan makircin shexan, yasan shigo-shigo ba zarfi irin na shexan yasan arautaki, da kugayar da shexan yake farautar mutane saboda haka da shexan ya ganshi sai yace ban mu tattara inamu-inamu ga wanda zaimana bukulunan yazo, domin bazai iya tunkararsa ya cuceshiba, sannan kuma mutukar jama’a suna tare dashi to shexan bazai iya nasara dasuba.
To wannan ce baiwar da Annabi (S.A.W) yake cewa sai wanda Allah ya nufa da alheri yake bawa wanda shaixan bazai iya yi masa komai ba.
‘HIKAYA’ wani bawan Allah shexan yayi masa irin shigo-shigo ba zurfi sai ya tsammaci ya zama na Allah ance idan yazo guri ya xaga ‘yan yatsunsa sai kawai aga zuma tana zuba dalala ta tsakanin hannu, sai azo da qwarya ayita tara anasha, sai ya xauka qaramace, to malaminsa da yake shi yasan sharrin ibilis yana da fikihu fiddini ba karatu kawaiba, da yaji labari, sai yace, Allah ya taimaki almajirinnan manu da Allah yasa ina da rai, ba dan haka ba sai ya gane dashi, yace bari muje mu ceceshi, da malamin nasa yazo sai zuma tayi ta kwarara, sai ya amsa masa da ainun (ai hakane) sai yace shi yasa muma mukazo musha albarka, ya buxe hannu sai ga hannun qandas, akayi-akayi zuma ta zuba, sai gashi ba zuma ba xalibin, sai malamin nasa yace dashi tashi kasan Allah, shexanne yake wasa dakai, mukuma idan muna gurin bai isa yazo ya kawo wani wasaba, saboda duk wani shigo-shigo ba zurfinsa mun sanshi, kai kwantansa muke tayarwa bai isaba, koma kaje kasan Allah, kayi maganin shexan, in ba hakaba ya halakaka gobe qiyama ka zauna gida xayatare dashi. To Annabi (S.A.W) ya nuna mana wanda Allah ya nufa da alheri shi yake bawa wannan ilimi.
Arabic

8) Sannan wannan ilimi Allah ya ajiyeshi ya zama shine fitila kuma shine jagora na imani, idan babu ilimi to baza’a iya imani ba, domin mutum zai zo yana ta abubuwa yana ta shirbicinsa amma baisan lokacin da zai warware duk abinda ya shukaba, kuma sanin Allah sa idan ba akan ilimi yayi ba kunfar kogine kawai, komai yazo sai yatafi dashi iska tana zuwa sai ta watsa shi, shi imani so ake sai akan ginshiqi mai qarfi ake xorashi sai ya zauna, shine iliminshi yasa acikin alqur’ani Allah Madaukakin Sarki yake cewa:
Arabic

“Bakuyi duba akan kawunan kuba, akan kanba idan kayi duba, kayi ilimi ka fahimci kanka”
To anan zakasan Allah (S.W.T) irin sanin da babu wanda ya isa yazo ya rabaka da wannan sanin, saboda kayl ilimi akansa, to sai da ilimi ake gane Allah (S.W.T), kuma abishi ayi imani mai karfi kuma dashine akejin tsoran Allah (S.W.T) dan hakane Allah yake cewa:
Arabic

”Kaxai acikin bayin Allah masu jin tsoransa sune malamai.”
Akwai qira’ar da take cewa:
Arabic

Fassarar wannan: “Acikin bayin Allah wandada Allah ya halitta, kuma yake jin nauyinsu malamai ne kadai”
Ita wannan qira’ar abinda take nunawa a cikin bayin Allah malamai suka xai Allah yake jin nauyinsu kuma yake jin kunyarsu, su kaxai wadanda basu da ilimi karabilo ne babu ruwan Allah dasu.
Sannan shi Ilimi shine garkuwa ta imani, shine abinda yake hana mutum fada cikin abinda zai rabashi da imani, ko yayi imani ya warware, kamar yadda idan yayi alwala, ya shiga bayan gida alwalarsa zata warware yan zunnan wawa jahili zai faxi kalmar da zata rabashi da imani nan take ta ja masa kisa, shi yasa ake cewa malami xayamasani mai tsentseni yafi jahilai dubu masu ibada, agurin shexan idan mutum kawai zai kama ibada yayi tayi, shexan da yazo kawai sai ya tureta, ya ruguzata, ta inda ma ba za a iya samo maikamarta ba, amma idan akwai ilimi sai ya kare imanin duk abinda zai ruguza abinka ba zai yuwu ba, kalmomin ka ba zasu jawowa mutum komai ba, aikace-aikacanka masu tsafta wanda ba zasu jawo rugujewar komai ba, malamai suna cewa:
Arabic

”Wato fasadine mai girma malami mai karakata alfarmar Allah tare da alfarmar ilimi, yaje yayi ta abinda yaga dama.”
Amma wanda ya fishi illa shine jahili mai ibada, “jahiline kungurmi kullum sai sallah, sai azumi, sai riqe carbi amman bai san komai ba.” Yace wannan yafi komai illa domin addini zai dinga yiwa karan tsaye yana lalatashi.
9) Ilimi shine sharadin nakarbar kowanne muqami na mulki, idan babu shi mutum bazai iya riqe kowanne irin muqami ba, sai dai yaje ya zama lebura, yayi ta share-share da goge-goge kawai a bashi. Amma ya riqe wani mukami A-A. Shi yasa Ubangiji yake gaya mana acikin kissar banu Isra’ila bayan wucewar Annabi Musa (A.S) Baqara: (aya ta: 246-247).
Sukace Annabinsu ya roqa musu Allah ya naxa musu sarki suje suyi yaqi, saboda Allah to da Allah ya basu sarkin, sai sukace: ya wannan zai shugabance mu alhalin mu muka fishi cancanta, gashi bashi da kuxi yana talakansa kawai sai yazo ya shugabance mu, sai Allah yace:
“Allah ya zabeshi ya fifitashi akanku ya bashi ilimi da lafiyar jiki.”
Saboda haka sai da lafiya sai da ilimi ake shugabanci, saboda haka ilimi shine sharaxin samun muqami ako’ina.
10) Ilimi shine yake bayyana farashin ayyuka daban-daban, domin kowacce ibada da Allah yace ayi sai da yayi mata farashi, wata tafi wata, to baza ka iya sanin farashin ibada ba sai kana da ilimi, idan kana da ilimi zakasan farashinta, da an xaga maka ibada za kace ga farashinta, saboda haka idan kasan wacce inkayi za’a baka daraja (100) da wadda in kayi za a baka (50) da wadda za a baka (10) in kana da ilimi nan take sai ka dauki wacce za a baka (100) xin, saboda kasan farashinta kasan darajarta kayi komai, to a harkoki na duniya idan ana neman kwararre idan akazo za’a yi siyayya shi ake sawa agaba, domin ya zava maka abu mai kwaliti, kuma ya neman maka rangwame gurin saye, idan kuma sayarwa zakayi shi zai nuna darajar abinka, ya nema masa qima, ya sashi yayi daraja. To haka Allah yake, shima masana su sukasan wannan ”Misali ka futa daga gida izuwa masallaci idan kana da ilimi ai karibanya masa niyya ta kai goma (10) kowacce Allah ya baka lada, amma jahili kuwa shida ya fita daga gida yace masallaci zani shi kenan, amma masani zai ce zani masallaci, a mazaunin almajiri zani, masallaci, duka wanda yayi min gyara zan karba, saboda haka sai Allah ya baka ladan,
Arabic_

zani masallaci a mazaunin mai kwaba idan naga abu ba dai-dai ba zanyi gyara, akai zan nuna, in naga wanda ba ayi na kirki ba zan nuna ayi nan kuma sai kashiga cikin

Nan sai Allah ya baka wannan ladan.
Sannan in zaka masallaci ka shafaturare domin Alummar usulmi su shaki kanshi ransu yayi dax, nan kuma sai Allah ya baka ladan farantawa musulmi,
Sannan kuma zan taf masallaci in zauna kafin liman ya fito dan neman murabidi, da Allah, domin Shugaba (SAW) yana cewa:

*       Ka zauna kana jiran lokacin sallah yayi Allah zai baka ladan murabadin wanda ya xaura xamara ya fita tsakanin iyakar musulmi da kafurai ya zauna domin kariya ga qasashen musilmi, irin ladan da Allah yake bawa waxannan na alheri, to irin  wannan zai bawa mai jiran sallah, to sai mutum ya tafi da wannan niyyar sai Allah ya bashi.
*       Sannan sai yace na tafi da niyyar yin jam’i domin raya sunnar Annabi (S.A.W) nan me sai Allah ya rubuta ladan.
*       Na tafi da niyyar sallah ta farillah wacce Allah Madaukakin Sarki ya falantamin sai Allah ya rubuta.
*       Ina son duk takuna a rubutamin ladan, kuma a kan karemin zunubi dashi a tafiyata masallaci da dawo wata to duk sai Allah yaba mutum wannan.
Amma idan mutum bashi da sani ya fitada niyya guda xayatak, shi kuma Ubangiji yana cewa damu acikin mutane akwai:
Muktasidun- wanda ya takaita a wajen aikin aiheri.
*       Akwai Zalimun Linafsihi- wanda ya zalinci kansa.
*       Akwai kuma Sabikun bil Khairat- wanda yayiwa mutane fintinkau awajan aikin aiheri, to haka akeso asamu.
To ilimi shi yake bawa mutum danar farautar wannan alherin, kuma ilimine  yake nuna masa darajar lokaci yasan lokaci kaza, aiki iri kaza yafi aiki iri kaza, lafazi iri kaza yafi iri kaza, to duk sai ya zabesu yayi tayi domin in antashi alqiyama sai ya zama yan birnin aljannah domin zai shiga cikinta. (Suratul: waqi’atu: aya ta 10-26).

‘yan birinin aljannah kenan suna kan gadaje wadanda akayi su da lu’u-lu’u da zinare da azurfa, ga sunan                                         sarakuna wadanda, sarautarasu, takai tsaiko sukaci suka sha, suka hau gado, suka kishingixa suka xau kafa suka xora xaya kan xaya sunayin sakace na isa bawai dan kawai fitar da wani abu daga cikin hakoriba.

Ga kuma yara qanana, sonata narai-narai, kamar lu’u-lu’u.
Akwai kofuna waxanda basu da mariki (saboda kofi mai mariki a aljannah azabace) sannan kuma ga butoci wadanda suke cike dagiya mai babuga, kuma ba tare da anyi wani ciwon kai ko anyi wata sokana ba. To wadannan sune ‘yan birnin aljannah.
Wanda Allah yace: marigaya-marigaya, masu ilimi su suke samun wannan, masu binsu kuma sune masu rayuwar karkara acikin aljannah, domin cewa yayi: (ayata 27-40).

Suna cikin magarya, domin inkaji ance za’a karkaxi magarya sai rayuwar karkara, da kuma shuke-shuken dabinai da inuwa shinfixaxxiya.

Wacce za a huta akarkashinta,

11) Sannan yana daga cikin falalar neman sani, dashi Allah yake horewa mutum tafarkin aljannah dodar. Yazo acikin wani hadisi wanda Imamu Turmizi da Abu-Dauda suka rawaito daga Uwaimir (Abud-darda’i) (R.A) Manzon Allah (S.A.W) yana cewa:

Fassara: Manzon Allah yace: Wadda duk ya yanke tafarki, ko ya dauki littafinsa domin ya tafi makaranta, yaje ya nemi sani wanda zai tsira a lahira, wanda anan duniya zai zama mutumin kirki, ya zauna da jama’a lafiya, ya tashi zai tafi wannan gurin, sai Annabi (SAW) yace da albarkar tafiya izuwa wannan karatun, Allah zai hore masa tafarkin izuwa aljannah. Malaman qarshen larabci suna cewa:

Wato idan akazo da suna Nakira (wato wanda ba a sani ba, kamar a Hausa kace, wane wani mutum dazu yazo, yana neman ka.
Wani mutum= wannan shi ake kira nakira, sukace idan akazo da suna nakira kuma da akayi gaba sai aka mayar da ita ma arifa, to na farkon ake nufi, kace ”wane wani mutum yazo yana nemanka kaga baka sanshiba kenan kuma ya zama nakira, sai kace dashi “to sai wannan mutum in yace nace nace maka kaza.”
To haka ta biyu “sai wannan mutamin xin da kace ya mayar dashi ‘MA’ARIFA’ yana nuna maka wancanxin da baisani ba shine ya bada wannan sakon.
Amma idan yace maka wani mutum dazu yazi, sai wani mutum yace abaka saqo, kasan ba wannan na farkon yake nufiba shine munufar
Idan kazo da nakira ka sake zuwa da nakira bana farko kake nufiba.
To ananan sai shugaba (S.A.W) yace:
Wanda yabi wani ta-farju
Sai yace
Baice
Ma’ana wannan tafarki ba shine na farko ba, tafiyarka ta neman ilimi da ban amma kuma dalilin tarce Allah zai hore maka wani tafarkin daban, bai ce Allah zai shigar dakai Aljannah ba.
Ya kamata mu fahimci wannan: -
Annabi (SAW) cewa yayi duk wanda yabi tafarkin neman ilimi, Allah zai heromasa tafarkin zuwa aljannah, domin shi ilimi abu biyu ne acikinsa “ ko ya zama hujja a gareka, ko kuma yazama hujja akanka.” In ya zama hujja agareka, shine za a sama maka wata hanya, kasamu muwafaqa, ilimi yazama na Allah hanyoyin Allah kake bi, wannan hanyar da kake bi to da ita Allah zai hore maka, kana mutuwa ana tashi ranar alqiyama, dodar zaka wucewarka aljannah wannan shine abinda Annabi (SAW) yake so ya nuna mana cewar wancan tafarki yana da bambamci da wannan.
Sannan kuma Annabi (S.A.W) xayafaxa mana haka sai yace mana sannan mala’iku kuma, suna shinfixa fuka-fikinsu ga me neman ilimi, idan ka fito zaka makaranta. Malaman hadisi sukace shugaba (S.A.W) a wannan hadisi sai yadinga yi masa taukidi yana qarfafa maganar, domin cewa yayi ‘INNAL MALA’IKATA’ haqiqa mala’iku LATADHA’U sai ya sake zuwa da wani LAMUL MUZAHLAKA: haqiqa mala’iku lallai suna shinfida fukafukansu (saboda abune na gaibu) Annabi sai ya qarfafashi da maganarsa mai gaskiyi mata taukidi dan ka yarda akwai.
Allah yana sa mala’iku su shinfida fukafukansu ga masu neman ilimi suna takawa saboda me, domin su masu fishine da fushin Ubangiji masu yarda da yardarsa, duk abinda Allah yakeso mala’iku zakaga suna rawar jiki akai, saboda haka abinda kake na neman ilimi Allah yana so, saboda haka mala’iku suke neman suyi gwaninta dornin su qara samun matsayi a gurin Allah saboda kai.
Tambaya: Amma mai yasa ba aji?
Amsa: Dalili shine domin ka tafi saboda Allah, sai Annabi (S.A.W) yace “wa innal alima” haqiqa malami, wanda yake da sani yake koyar da bayin Allah, duk halittar da take sama gaba xaya, data kasa suna nema masa gafara a gurin Ubangiji, wanda Annabi (S.A.W) yace asama, babu gurin da zaka saka ‘yan yatsunka huxu face akwai mala’ika duk faxin sama mala’iku ne suka cikata damqar nishi take saboda tsananin cikar da tayi, amma Annabi (S.A.W) yace duk abinda yake cikinta yana haba-haba damai ilimi, yana ta rawar qafa dashi saboda yasan waye shi a gurin Allah.
Sai da Annabi (S.A.W) ya sake cewa “INNA- sannan yace LAYASTAGAFIRU” yace dukkan halitta da take qasa yace harda kifi da yake ruwa (domin halittar cikin ruwa da tururuwa wacce take yawo a cikin raminta amma tana istigifari ga mai neman ilimi.
Amma maye dalilin dayasa malamai suka sami wanan daraja duk halittar sama data qasa suke haba-haba dasu? Sai Annabi (S.A.W) yace. AL-ULAMA’U WARASATUL ANBIYA’I” malamai sune magada Annabawa, sune waxanda in kazo kafaxi Magana da karfi a gabansu ko ka shekara (70) kana ibada sai Allah ya rusheta, ko waye kai baza ka xaga murya a gaban malami ka faxi abinda ranka yakeso ba, sai Allah ya rusa ibadarka, saboda waxanda suke gadar haka Allah zakmusu suma kuma haka Allah zai yi musu. Sai Annabi (S.A.W) yaci gaba “INNAL ANBIYA’A LAM YU WAR’RATHUL DINARRA WALA DIRHAMIN” su Annabawa basu bar gadan basubar gadan azurfaba, ilimi suka bari shine gadansu, wanda duk Allah yasa ya sami ilimi to wannan shine ya sami babban rabo daga cikin rabon da Allah_yake rabawa acikin al’ummarsa, gaba daya) to wannan hadisin shi kaxai ya isa ya wadatar damu, akan faiaiar Nimi da kuma martabar malamai.
11) Yana daga cikin martabar ilimi da masu shi, shine fadan Shugaba (S.AW):

Fassara: “Duniya da duk abinda yake cikinta babu abinda yake da qima agurin Allah, (duk ababan la’anane agurinsa yace waxanda suke da qima agurin Allah, shine ZIKIRULLAHI da abinda ya shafeshi kamar su Sallah, Azumi, Sada zumunci, gaskiya rikon amana, rike alkawari.
Sai kuma malami mai koyarwa da kuma dalibi mai zuwa ya koya.
Wadannan sukaxai suke da ilimi agurin Allah kawai amma in bandasu komai kake gani acikin wannan duniya bashi da wani qima agurinsa, da abin duniya yana da qima guda xaya agurin Allah ko da dai-dai da fukafukin sauro, to da Allah bai bawa kafuri ruwa koda magwarwa xaya a duniya ya shaba, baya da qima shiyasa ya saka ta haka, waxanda suke da qima a gurinsa sune waxanda Annabi (S.A.W) ya lissafa.

AKHALA KIYATUL MU AL-LIM
Akwai xabi’u da halaye da akeso masu ilimi su siffantu dasu saboda da sune ilimin yake amfani
Sune kamar haka:
1.       Ash-shi’unufil mas-uliyyah
Ya dinga jin cewa akwai nauyi da amana akansa wannan ilimi da Allah ya bashi ba abanza ya bashi ba, badan kansa ya bashi ba, ya bashine saboda bayin Allah gaba xaya shi yasa Allah yace:

“karanta da sunan Ubanglnka wanda yayi hallita”
Kasan karamcin da Allah yayi na baka ilimi ya bakane dan amfanin sauran halitta, ilimin nan ya zama rahama gareka, ya zama rahama ga sauran halitta, ba kazama mai amfani dashi wajan cutar da jama’a ba, da kuma yin bukatar kanka ba, wannan itace siffar masani ta farko ya zama ba kansa yake kulawa da shiba a nauyin da yake kansa, na wannan, amana ta ilimi ita yake qoqarin ganin cewa sai ya sauke.
Wannan masa’uliyyar irinta Imamu Ahmad bn Hambal (R.A) ya gamu da ita, wanda yake shine Imamu Ahlussunnah wanda yake ya haddace hadisin Arinabi ya kai miliyan xaya da dubu dari uku da doriya. Ko wanne da isnadina zai kawo maka shi tar kamar Fatiha, to lokacin da akazo da rigimar Khalful qur’an, sai aka nemi da lallai sai ya yarda da wannan sai yace” ai kuwa haka bata yiwuba, sai da ya rasa ransa, akan hakan, akayi-akayi har aka kaishi kurkuku, babu abinda ba’a yi masaba sai da takai ranar da aka sakeshi daga cikin kurkuku sarkar da take jikinsa wadda aka xaureshi da ita ana kwanceta. Naman jikinsa yana zabtarewa yana faduwa, amma yace ya yarda da wannan azabar, akan yaci amanar Annabi.
Domin a wannan lokacin da Immau Ahmad ya yarda da wannan da Al-umar Annabi (S.A.W) ta halaka tun daga wannan lokacin har izuwa ranar tashin alkiyama.
Shine “Ash-shu’uni ful masa uliyyah”

Masani ya ture ya zama juji dukkanin wahala ya xauka domin al’umma ta tsira; haka akeso masani ya sami wannan.


2.       AL-AMANATUL ILIMIYYAH:
Amana ta ilimi itace ya zama iya abinda malami ya sani, iya kansa kawai zai tafi, kar ka yarda ba ka san abuba ka xora mutane akai, domin tserar da addini tare da mutane daga fadawa cikin halaka. Wata rana Imamu Maliki (R.A) an turo wasu mutane daga wani gari mai nisa, izuwa gareshi, domin suyi masa wasu tambayoyi akan mastalar addini musulunci, waxannan mutanen sukwana anan sutashi, har suka zo madina yazo da tambayoyi guda saba’in (70), ya karanta tambayoyinsu.
Imamu Malik ya amsa masa uku (3) sauran kuwa, Maliku yace “Bansani ba” Yace me zan gayawa mutane?” yace “in kaje kace musu Maliku baisani ba.” Wanna itace siffar masana.

Amma wanda bai sani ba da an tambayeshi abinda bashi da sani akai, sai yace in ban bada amsa ba ai girmana zai faxi, nan danan sai ya bayar da Amsar ba dai-dai ba yayi xinki a varaka, karshenta a cikin wandanda sukayi masa tambaya akwai wanda yake da sani yana amsawa ba dai-dai ba, zai ce wannan mahaukaci ne kawai, ya amsa abinda ba haka yake ba sai girmansa ya zube, kuma abinda ake gudu kuma ya faru, amma dayace “ban sani ba” shikenan qima ta tashi Allah ya yarda yana da ilimi, kuma yana da amana ta sani.
Sannan yazo yayi bayani, zai dangana ra’ayi ga masu shi, idan ya san mas’ala ta savani ce, zai futo ya fadeta yace ”ga ra’ayin su wane ga arayin su wane gashi-gashi in akwai tarjihi, ana rinjayar da xaya kan xaya to sai ya fada.
Amma wanda bashi da siffar ilimi, in yana da ra’ayi, to ra’ayin daya karkata akai to shi zai dinga dora mutane sai ya rufe waccen ra’ayin, harma daga karshe ya dinga nunawa ra’ayinsa duk wanda bai bi wannan ra’ayin ba to fa ya kafurta, to duk wanda yake da wannan bashi da amana ta ilimi.
3)      AT-TAWADHI’U
Yana daga cikin siffar masana (Malamal) kaskantar da kai.
Masani tawari’u yakeyi saboda shugaban masana na duniya baki xaya shine Annabi (SA.W) babu wanda ya fishi Tawari’u.
Lokacin da Adiyyu Dan Hatimuddai yazo Madina ya fara gamuwa da Annabi (S.A.W) ya karveshi hannu biyu-biyu yace “Adiyyu ne?
Annabi yace “Naso ace naga mahaifinka, duk da cewa mahaifinsa a jahiliyya HATIMUDDAI shine mutumin da aka sameshi me kyauta, azamanin Larabawa na jahiliyya bata tabasamin mai kyauta kamar saba,” wannan dabi’artasa ta kyauta ita Annabi yayi sha’awa yace ”Naso ace nayi musharaka dashi,” sai ya karbeshi suka gaisa, su kayi maganganu, sai yace to mutafi gida, sun taho zasu tafi gida, sai yaga Annabi suna lafita in yarinya ‘yar karama ta fito ta tsai dashi sai ya tsaya, sai tayi magana in tagama, sai Annabi (S.A.W) yace kin gama? In tace A, sai suyi gaba, sai yaga wannan talaka ya tsai dashi, wannan masakin  ya tsai dashi, sai Adiyyu yace” to daga nan sai nasan wannan ba basa rake bane, Annabi ne, tun da, yana da kasqantar da kai, da sukaje can gidan Annabi, sai Annabi ya tuve mayafinsa ya shinfida masa yace to zauna, sai yace a’a kai zauna, sai Annabi yace “ai kaine baqona saboda haka kai zan girmama, sai Adiyyu yace to daganan na sallama masa nasan cewa wannan Annabi ne ba duniya yazo nema ba.”
To masani shi yake tawari’u ya kaskantar da kansa. To Allah ne yake xaukakawa idan ya daga darajarka a AL-MALA’ULA ALA, anan duniya kowanne yazo ya taka ba komai, amma acan an sanka idan alqiyama tazo sai Allah ya nuna menene darajar mai ilimi.
To don haka ba’a yarda da girman kai agurin malamai ba.
4)      AL-IZZATUL ILIMIYYAH
Jin izza ta sani, shine masani kada ya yarda a tozarta ilimi, a’a shi ba kansa yake kalloba, qimar ilimi yake dubawa, dan baiwace ta Allah kuma gadan Annabawa ne, shiyasa ba’a yarda atozartashi.
Shi yasa lokacin da Imamush-shafi’i ya kamala karatunsa agurin1mamu Maliku zai tafi, wasiyar da yayi masa a mazauninsa na mamaminsa sai yace, “inayl maka wasiya da abu guda uku (3)
a) In ka tashi zama kusa da mai mulki (ma’ana wani abu ne larura ya jawo ka zauna tare da shi) to karka yarda ka zauna gaka gashi, ka dinga barin tazara tsakaninka dashi, yace “wannan na yi maka wasiyya karike wannan.
To me Imamu Maliku yake nufi da wannan shine domin acikin fada akwai ‘yan morin wadanda suka isa agurinsu, idan sukazo mai mulki bazaiji kunyar cemaka matsa wannan ya zauna ba, to su agurinsu duk randa aka yiwa mai ilimi wannan to an wulaqanta ilimi, saboda haka baihalatta mai ilimi ya ban wannan ta sami ilimi ba.
b) karka yarda kashiga fadar kowanne irin  mai mulki, sai kasan acikin fada akwai wanda ya sanka, domin in babu sai an nemi kayi bayani kanka kai kuma bazaka fito kayi bayanin kanka kace kai neman ilimi in kaza ba in kaza to su kuma basu san qimar wannan ilimi ba, karshe abinda zasu yi maka “wulaqanci” shi kuma ilimi ba’ayi masa wannan, “Abu-Hazim ya taba shiga gurin xaya daga cikin halifofin banu Umayyah, bayan an kammala aikin hajji Halifa yasa har sa’a masa kujera kusa da ka’aba ya zauna, ga karagu manya, mutane sun kewaye anata fadanci sai ga Abu-hazim ya shigo, to hanunnunsa xaya ashanye yake, qafarsa xaya itama a shanye take, yana girgawa, kuma gashi idansa xaya amma kuma “Masani ne,” yana shigowa da Khalifa ya ganshi, kawai sai ya tashi daga karaga. ya bashi ya zauna, da ya zauna sai yace “ina yl maka wasiyya ka kula da masallacin Annabi (SA.W) ka kuma kulada Haramin Makkah, domin waxannan sune manyan masallatai agurin musulmi sai yace ”in allah ya yarda zan kula bazan bari su tozarta ba, sai yace ”ina yi maka wasiyya ka kula da ’yayan sahabbai Muhajiruna (wadanda su kayi hijra) da kuma ‘yayan Ansaru domin iyayensu su suka miqe suka zage dantse har musulunci ya kafu har kai kazama halifah sai yace ”In allah ya yarda ’ya’yan Muhajiruna da Ansaru babu wanda zai tozaarta ba wanda zai wahala zan kula dasu, sai yace ina yi maka wasiyya ka kula da al’ummar Annabi (S.A>W) domin Annabi yana son al’umarsa kuma saboda ita yayi duk abinda yayi, gashi kuma saboda haka kazama Khalifa sai yace ”in Allah ya yarda babu wani mutum daga acikin al’ummar Annabi da zan bari ya tozarta zan kula da haqqinsa daya gama, sai Khalifa yace dashi ”To kai kuma me kakeso ayi maka?” sai Abu-hazim yace ”Allah shi zai yimin amma ba kai ba.
To wannan itace izzah ta ilimi. Shi kansa khalifah da kansa yace “zaka hiyal Hibbah” wannan itace kamewa, shi yasa daya ganshi ya sauka daga kujerar ya bashi ita, saboda yasan bashi da kwaxayi, kuma yasan girman abinda yake xauke dashi.
Arabic


5)      AL-AMALU BIL MUKHTAMUL ILI
          AIKI DA SANI
Kar mutum ya zama na yana da ilimi amma kuma ya takeshi. Kaji ana cewa “aiwane sani ya take, abinda ya karanta ba dashi yake amfani ba, to mai ilimi ba asanshi da wannan ba, abinda ya kamata kuma ya fahinta dashi yake aiki, to wannan shi ake bukata masani ya samu, idan ya samu sai Allah ya taimakeshi, ya daga Alkadarinsa har izuwa aljannah fiddausi a ala, wanda muke roqon Allah yayi mana ganda katar da dacewa dasu ameen.
ABUBUWAN DAYA WAJABA AKAN MAI NEMAN ILIMI
Shi kuma mai koyon karatu:
1)    Kyakyawar niyyah, yana son ya koyi ilimi ne saboda Allah, domin ya bautawa Allah, gyargyardan yadda zai iya yadda Allah yakeso.
*       Kuma yana son yayi ilimi ne domin ya raya Addini domin idan babu ilimi addini ba zai rayu ba
*       Kuma yana son yayi ilimi ne domin ya g4a Allah godiya akan ni’imar hankali day-a bashi.
2)    Tsoran Allah: - domin Allah yace acikin suratul Bakara aya ta: 22)
Arabic

Kuji tsoron Allah sai Allah ya sanar daku”.
Duk lokacin da kaji tsoron Allah, to sai Allah ya sanyawa ilimin albarka.
3)    Yin Aiki da duk abinda ka sani domin Manzon Allah (SAW) ya ce:
Arabic

Wanda duk yayi aiki da abinda ya sani sai Allah ya bashi gadon ilimi da bai san shiba duk inda ka koyi mas’ala xaya in dai kayi aiki akai, sai Allah ya nusar da kai tara sai ta zama goma (10) shi yasa Sahabban Annabi (S.A.W) a zamaninsu idan suka koyi aya xaya basa koyarta biyu har sai sunyi aiki da ita sannan suci gaba, domin Abdilahi bn Umar (R.A) ance saida ya shekara takwas, sannan ya haddace suratul Bakara gaba dayanta domin yana tafiyane da Haddar da aikinta, da haddar da aikin to haka sahabbai suka dingayi, kuma da aikine ilimi yake tsayawa.
4)    HUSUNULISMA’A
Kyakyawan sauraro, idan anzo karatu mutum ya tattara hankalinsa gaba xaya ya zama abinda yazo yi xinnan shine a gabansa.
Shehu Usmanu bn Fodiyo, ance sun zauna acikin garin Katsina gurin wani malaminsu domin xaukar karatu ance sai suka shekara a qarkashin wata bishiya amma basu san ko bishiyar mecece ba, saboda su kawai karatu ne a gabansu, sai randa xan itaciyar ya nuna ya fado akan littafinsu sannan suka xaga kai sukaga ashe itaciyar aduwace.
To haka akeso mai koyon karatu ya duqufu wannan karatun shine kadai agabansa in yazo kawai tattara hankalinsa zai yi gurin, xaya gurin malamin, ba rarrabashi zai yiba, (abinda ya kawoshi da ban, abinda yake aikatawa kuma daban ba).
Lokacin da Imamu Maliku (R.A) yana Madina ya zama rana ta ilimi ko daga ina ana zuwa, Yahaya ya taso tun daga Andulus (Spain) a yanzu, ya kwana ya tashi ya kwana ya tashi yazo har Madina, da yazo Madina yana koyon karatu gurin Imamu Maliku (R.A) rannan sai giwa ta shigo garin Madina da rana tsaka, sai duk almajirai suka dare suka tafi kallon giwa ga giwa har cikin gari, ana bin giwa ana kallo, ita kuma tana tafiya, ya zamo makaranta ta dare babu kowa sai Yahaya shi kaxai, ne a zaune Imamu Malik yana zaune, sai Imamu yace dashi Yahaya kai bazaka tafi kallon giwarba?
Sai ya amsa masa “dacewa ai ga giwata a zaune, saboda kai na baro garinmu, badan waccen giwar ba, kumama guda nawa nagani a hanya? Saboda haka bazan bar abinda nazo yi sabodashi, natafi izuwa abinda bashi ya kawoni ba, to sai Imamu Malik yasa masa suna HAKIMUL ANSULUS.
5)    IYA TAMBAYA:
Ana so dalibi ya zama mai iya tambaya wadda idan kayi ta zaka qaru wadda bata da amfani ba abinda da jahilcinsa da saninsa duka dayane to kada mai neman ilimi ya qarar da lokacinsa a wannan
Arabic

Kullum so ake ka tambayi abinda, kasami amsarsa, to aqadarin ka ya karasama, a fagen ilimi, kuma ka fahimta kuma ka samu abinda za kayi to haka akeso mai neman sani ya kasance.
Shi yasa Sahabban Annabi (S.A.W) suka bar mana darasi wajen wannan iya tambayar, lokacin da Shugaba (S.A.W) yace da sahabbansa

Arabic

Wannan zuciyar da kuke gani tana tsatsa kamar yadda karfe yake tsatsa. Saboda su gwana yene, kumak qwararru, basu tambayeshi ta yaya zuciya take tsatsa ba, sai suka ce masa ya-rasulullah to menene maganin tsatsar?
Sai yace dasu:
“Karatun alqur’ani shine maganin, kaga sun sami magani.
6)    CIN HALAK:
Domin dukkanin mai neman karatu sai yaci halak sannan zai sami ilimi, kuma aji tsoron Allah kale-kallon haramun da abubuwa da miyagun halaye duk sai an rabu dasu sannan ilimi zai samu.
Imamu Shafi’I (R.A) ance yadda kasan photocopy haka kwakwalwarsa take duk abinda ya saurara to nan take zai haddace shi ance “in zai karanta littafi mai shafi biyu to sai ya rufe xaya shafin sannan zai iya karanta shafin farko idan kuwa ba hakaba to gabaki xaya shafi biyun zai haddace. To rannan da yazo yayi karatu sai yaga kasa haddacewa, sai ya tabbatar da lamarin ya lalace, sai ya tafi gurin malaminsa Malam WAKI’U, yace masa “Haqiqa na fara samun tangarxa a wajan qwaqwalwata, sai malamin nasa yace “to duk yadda akayi ka savi Allah.” Kani sanci sabon Allah sai ka tsira, to shine da kansa yake cewa:
Arabic
Fassara:
Yace: “Nakai kamar lalacewar Jadda girim waki’u
Sai ya shiyar da ni izuwa barin savon Allah da nisantarsa,
Kuma yace “ilimi haskene na Allah da yake bayar dashi baiwa ga wanda yaso,
Shi kuma baya bayar do wannan bawar go mai sabo, in ya bawa mutum tarin karatu yaja ya fassara in dai bashi tsoron Allah to wannan ba ilimi bane karatu ne kawai to don haka ilimi saida tsoron Allah ake samunsa.
Sai Imamu Shafi’I yace “sai naje nayi ta binkice, dana gama binkice sai na sami, ashe wata baiwar Allah ce garin ta xauko wani abu, sai mayafinta ya yaye hannun ta yafito har gwiwa, wannan hannun ya gai shine ya jawo masa wannan matsalar fahintar iliminsa.
7)    Sayyadina Aliyu dan Abidalib (R.A)
Arabic
Sayyadina Aliyu yace:

Kayi sani yakai mai neman ilimi, baza kasami ilimi ba saida abubuwa guda (6) yanzu zan baka jerinsu a bayyane:
1.     Kaifin hankali
2.     Kwadayin ilimi
3.     Hakuri
4.     Guzuri (Kudi)
5.     Koyarwar Malami
6.     Tsawon Zamani
8)    GIRMAMA ILIMI DA MA ABOTANSA (MALAMAI)
Mai neman ilimi bazai samu malami ba, kuma iliminsa bazai zama mai amfani ba, sai ya girmama shi, shine abinda malamai sukace:
Arabic

Fassara: Duk wanda ya kai wani matsayi to bakai gareshi saida ganin girman manya, wanda kuma ya gaza kaiwa ga wannan matsayi bai gazaba face da rashin ganin girman manya (affarmarsu).
Yana daga cikin girman ilimi girmama malami, Sayyadina AIiyu (K.W) yana cewa:
Arabic

Fassara:
“Haqiqa ni na zava wa ga duk wanda ya sanar dani Harafi koda guda xayane, in yaso ya sayar dani, idan yaso ya ‘yan tani, in ya so ya bautar dani.”
Wani mai fida yanada, cewa “Na gane cewar mafi cancantar haqqi shine haqqin malami.
Mafi zama wajibi akan dukkan musulmi ya kiyaye.
Malami ya cancanci ayi masa kyautar girmamawa ma ya koyar da harafi xaya abashi dirhami dubu (1,000).
Haqiqa duk wanda ya sanar da kai harafi xayana abinda kake bukata na addini, to ya zama uba agareka acikin addini.
          An rawaito cewar Al-hafizu Abdul-Faraji Ibni Jauzi ya halarci makarantar Shehu Abdul-qadir Jilani (R.A) (a qarshe qarshen rayuwar Shehu Abdul-kadir) ya zuana a locakin da Shehu yake fassara wata aya daga cikin al-qur’ani, sai wasu waxanda suka san Ibmil Jauzi, sukace ala gafarta Mallam kasan wannan fassarar? Sai ya amsa musa dace wa ”Naam” (nasanta), sai Shehu ya sak ecewa bayan wannan tana da wata fassarar, masu tamabaya basu gushe suna tambayar Ibinil Jauzi ba da cewa ko yasan wanna fassarar, shi kuma yana amsa musa daceawr nasani, har sai da Shehu Abdul-Kadir yayi mata fassarara kala goma sha huxu (14) Ibinil jauzi yana cewa nasani, sanna Shehu Abdul-kadir ya sake cewa bayan wanna tana da wata fassarar har sai da ya kawo fuskokin fassarar wanna ayar sau arba’in (4) masu tambaya suna tambaya Ibinil Jauzi kasanta yana cewa ”WALLAHI LAADARI”. Shehu Abdul-kadir (K.S) ya kawo Iara (26) wadda Ibnil Jauzi bai santa ba, mai ruwaya yace ”gaba xaya mahalarta wannan makarantar suka ximauce, Al-habizu Abul-Faraji Ibnil Jauzi yace ”INNAHU ILIMUL AHALUL LAHI” haqiqa wanna ilimin mutan Allah ne, Allah yayi gaskiya da yace

Bai gushe ba yana ta mai maita ta.